Akalla ’yan bindiga tara ne suka sheka lahira a wani gumurzu da suka da ’yan banga a yankin Azza dake karamar hukumar Lapai, a jihar Neja.
Aminiya ta gano an yi dauki ba dadin ne a ranar Lahadi, yayin da wasu mutum biyu suka hadu a daji domin kai kudin fansar ’yan uwansu.
Wata majiya da ta shaida mana yadda abun ya faru, ta ce ’yan bangar sun yi shiri na musamman ne inda suka farmaki ’yan bindigar.
- ‘Yan bindiga sun kwashe ‘yan Maulidin kasa dake hanyar zuwSokoto
- Izzarso : Sun saki zafafan Hotuna a gurin birthday din Umar hashim
An dauki tsawon awanni ana dauki-ba-dadi, wanda ya yi sanadin rasa hallaka ’yan bindiga tara.
Wani mazaunin yankin Gulu, yayin tattaunawa da wakilinmu ta wayar tarho a ranar Abasar, ya bayyana, yadda wata mata ta kubuta tsirara daga hannun ’yan bindigar, sakamakon ruwan sama mai karfi da aka yi.